Kwankwaso Ya Bayar da Guraben Karatu 148 Ga Hazikan Daliban Najeriya

0 Northerners - AREWARMU | Tiktok Song - Hausa Novel  - Artists
 

Gidauniyar Kwankwasiyya Development Foundation ta zaɓi dalibai 148 daga jihohi 36 na Najeriya da kuma Babban Birnin Tarayya (FCT) domin samun tallafin karatu na kashi 100 cikin 100 a Mewar International University Nigeria.

Shirin ya mayar da hankali ne kan fannonin karatu masu muhimmanci kamar injiniya, kimiyyar kwamfuta da gudanar da harkokin kasuwanci, domin samar da kwararru da za su taimaka wajen ci gaban kasa.

Daliban da aka zaba za su bi matakan tantancewa da tabbatar da cancanta kafin a ba su guraben karatun. Haka kuma, an ware gurabe hudu daga kowace shiyya domin tabbatar da adalci da bai wa kowa dama.

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya dade yana tallafa wa dubban dalibai wajen samun ilimi, inda a wasu lokuta ma ya sadaukar da kadarorinsa domin taimaka musu. Wannan sabon shiri na daga cikin kokarinsa na ci gaba da bunkasa ilimi da gina hazikan matasa, musamman a wannan lokaci da kudin karatu ke ci gaba da karuwa.

Wannan mataki ya kara nuna kudurin Kwankwaso na inganta ilimi da samar da damammaki ga matasan Najeriya domin su zama masu amfani ga kansu da kuma al'ummarsu.

Tags :-

Post a Comment

0 Comments
We use cookies to improve your experience on our website. Learn More
Ok, Go it!