Najeriya Ta Kashe Sama Da Ýan ta'ada 13,500 A Cikin Shekara Daya
0
June 12, 2026
June 12, 2026
Najeriya Ta Kashe Sama da 'Yan Ta'adda 13,500 a Cikin Shekara Daya
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samu gagarumar nasara a yaƙin da take yi da rashin tsaro, inda jami'an tsaro suka kashe sama da 'yan ta'adda 13,500 a faɗin ƙasar cikin shekara guda.
A cewarsa, an samu wannan nasara ne sakamakon ƙoƙarin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da kuma sabbin matakan da gwamnati ta ɗauka domin daƙile ayyukan ta'addanci, garkuwa da mutane da sauran laifukan da suka addabi ƙasar.
Tinubu ya kuma ce dubban mutane da aka yi garkuwa da su sun samu 'yanci, yayin da jami'an tsaro suka kama da dama daga cikin masu aikata laifuka tare da kwato makamai masu yawa.
Shugaban ya bayyana hakan ne a sakonsa na ranar Dimokuraɗiyya, inda ya jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, tsaro da walwalar al'ummar Najeriya.
Sai dai wasu masu sharhi na ci gaba da kira ga gwamnati da ta ƙara ƙaimi wajen magance matsalolin tsaro da har yanzu ke addabar wasu yankunan ƙasar.
Tags :-
