Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani na Najeriya, Prof. Isa Ali Ibrahim Pantami, ya koma jam’iyyar PDP bayan ficewarsa daga APC a jihar Gombe. Rahotanni sun bayyana cewa Pantami ya samu tikitin takarar gwamna na PDP domin zaben shekarar 2027
Wannan mataki ya jawo cece-kuce a siyasar jihar Gombe, musamman ganin cewa Pantami na daga cikin manyan jiga-jigan APC a baya. Ana zargin rashin gamsuwa da yadda aka gudanar da tsarin fitar da dan takarar APC ne ya sa ya dauki wannan matsaya.
Bayan bayyana komawarsa PDP, dubban magoya baya sun nuna farin ciki tare da bayyana cewa Pantami na da kwarewa da hangen nesa wajen kawo cigaba a jihar Gombe. Shi ma Pantami ya bayyana cewa burinsa shi ne yi wa al’ummar jihar hidima cikin gaskiya, adalci da ci gaba.
Sai dai wasu ‘yan takarar PDP sun nuna rashin jin dadi kan shigowarsa cikin jam’iyyar, inda suka ce akwai bukatar a bi doka da ka’ida wajen tsarin takara.
A yanzu haka dai siyasar Gombe ta kara daukar zafi, yayin da jama’a ke ci gaba da sa ido kan yadda fafatawar 2027 za ta kaya.
